Shugaban Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Shugaba Ramaphosa a Johannesburg

top-news

Zaharaddeen Ishaq Abubakar, Katsina Times 

A ranar Alhamis, Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya yi taron sirri da Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, a Johannesburg, Afirka ta Kudu.

Kafin taron sirri da aka yi a Hotel Radisson Blu a Johannesburg, Shugaba Ramaphosa ya godewa Shugaba Tinubu bisa halartar bikin rantsar da shi a wa'adin mulki na biyu.

"Na gode sosai da ka halarci bikin rantsar da ni. Na yi farin ciki matuka ganin dan uwana a wurin bikin," in ji Shugaban Afirka ta Kudu.

Shugaba Tinubu ya nuna cewa jawabin Shugaba Ramaphosa a wurin bikin rantsar da shi ya bayyana mafi yawan matsalolin da kasashen Afirka ke fuskanta da bukatar karin hadin kai tsakanin shugabanni da 'yan kasa domin samar da mafita.

"Na ji dadin jawabin ka sosai a wurin bikin. Na ji dadi sosai da sauraron ka. Muna da matsaloli da dama da muke bukatar yin aiki tare. Bikin ya kasance mai kyau," in ji Shugaba Tinubu.

Shugaba Ramaphosa ya sake lashe zaben shugaban kasa a karo na biyu a ranar Juma'a, 14 ga Yuni, 2024, bayan yarjejeniyar kafa gwamnatin hadin kai tsakanin jam'iyyar African National Congress (ANC) da Democratic Alliance.

NNPC Advert